Numbers 24:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَمَرْ ذَاكِ يَݣُونْتَ أَ مِيڧٜىٰ، كَمَرْ سَرْكِنْ نَمُواْمِنْ دَاجِ، وَ ذَيْ ڟُواْكَنٜىٰشِ؟ يَا إِسْرَٰٓءِيلَ، دُكْ وَنْدَ يَأَلْبَرْكَثٜىٰكَ، ذَاعَ أَلْبَرْكَثٜىٰشِ؞ دُكْ وَنْدَ يَلَعَنْتَكَ، ذَاعَ لَعَنْتَشِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Al'ummar tana kama da ƙaƙƙarfan zaki Sa'ad da yake barci, ba wanda zai yi ƙarfin hali ya tashe shi. Duk wanda ya sa muku albarka zai sami albarka, Duk wanda ya sa muku la'ana zai sami la'ana.”