Numbers 3:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Nadab da Abihu suka fāɗi suka mutu a gaban Ubangiji a Hamadar Sinai a sa’ad da suka ƙona turare da haramtacciyar wuta a gabansa. Ba su kuwa da ’ya’ya; saboda haka Eleyazar da Itamar kaɗai suka yi aiki firist a zamanin mahaifinsu Haruna.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا نَدَبْ دَ أَبِهُ سُنْ مُتُ أَغَبَنْ يَهْوٜىٰهْ أَ دَاجِنْ سِنَيْ، أَ لُواْكَثِنْ دَ سُكَ مِيڧَا وَ يَهْوٜىٰهْ وُتَرْ دَ بَتَدَاثٜىٰبَ دُواْمِنْ هَدَايَ؞ سُنْ مُتُ بَا یَیَ؞ سَبُواْدَ حَكَ عٜىٰلٜىٰيَظَرْ دَ عِتَمَرْ سُكَيِ حِدِمَرْ ڢِرِسْتِ دُكَنْ ݣُونَكِنْ رَايُوَرْ بَابَنْسُ هَٰرُونَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Nadab da Abihu sun mutu a gaban Ubangiji a jejin Sinai, a sa'ad da suka ƙona turare da haramtacciyar wuta. Sun mutu, ba su da 'ya'ya, saboda haka Ele'azara da Itamar suka yi aikin firist su kaɗai a zamanin mahaifinsu Haruna.