Numbers 8:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Cikin dukan Isra’ilawa, na ba da Lawiyawa kyauta ga Haruna da ’ya’yansa, su yi hidima a Tentin Sujada a madadin Isra’ilawa, su kuma yi kafara dominsu saboda kada annoba ta bugi Isra’ilawa sa’ad da suka je kusa da wuri mai tsarki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَغَ ثِكِنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا كُوَ نَبَا هَٰرُونَ دَ یَیَنْسَ ݣَوْتَنْ لَوِيَاوَا دُواْمِنْ سُيِ وَسَوْرَنْ یَیَنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا حِدِمَ عَتٜىٰنْتِنْ سَدُوَ؞ ذَاسُ كُمَيِ هَدَايَ تَطَوْكَرْ أَلْحَكِنْ ذُنُوبِنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا، دُواْمِنْ كَدَ بَلَعِ يَڢَاطُواْ عَكَنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا عِدَنْ سُكَذُواْ كُسَدَ وُرِنْ ذَمَنَ مَيْ ڟَرْكِے؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Daga cikin Isra'ilawa kuwa na ba da Lawiyawa ga Haruna da 'ya'yansa maza don su yi wa Isra'ilawa hidima a alfarwa ta sujada, su kuma yi kafara dominsu don kada annoba ta sami Isra'ilawa sa'ad da suka kusaci alfarwa ta sujada.”