Numbers 9:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كُواْ دَ ݣُونَكِے بِيُ نٜىٰ، كُواْ دَ وَتَا طَيَ نٜىٰ، كُواْ دَ شٜىٰكَرَا طَيَ نٜىٰ، دُكْ لُواْكَثِنْ دَ ڧُنْشِنْ غِرْغِجٜىٰنْ يَڟَيَ عَبِسَ تٜىٰنْتِنْ، جَمَعَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ ذَاسُيِ تَذَمَ أَ ذَنْغُوانْ، بَذَاسُ تَاشِبَ؞ عَمَّا عِدَنْ ڧُنْشِنْ يَتَاشِ، سَيْ سُو مَا سُتَاشِ سُكَامَ حَنْيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ko kwana biyu ne girgijen ya yi, yana zaune a bisa alfarwar ko wata guda, ko fi, sai Isra'ilawa su yi ta zamansu a zangon, ba za su tashi ba. Amma in ya tashi, sai su kuma su tashi.