Psalms 17:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so; ’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa ’ya’yansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا يَهْوٜىٰهْ ، دَغَ یَنْ أَدَمْ، ثٜىٰثٜىٰنِ، دَغَ مُتَنٜىٰنْ دَ دُونِيَرْ نَنْ نٜىٰ أَبِنْدَ سُكٜىٰ دَشِ؞ حُكُنْتَسُ دَ ثِكَكّٜىٰنْ أَبِنْدَ كَشِرْيَ مُسُ؞ بَرِ یَیَنْسُ سُغَاجِ إِسَشّٜىٰنْ شِرِنْ، حَرْ مَا يَكَيْ كَنْ جِيكُواْكِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ka cece ni daga gare su da ikonka, Ka cece ni daga waɗanda suke da duk abin da suke so a duniyan nan, Ka hukunta su da wahalar da ka shirya musu, Ka sa har 'ya'yansu, su ma, ta ishe su, Wahalar da ta ragu kuma, ta sami jikokinsu!