Psalms 7:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَرِ كَڟَيْ دَ مُغُنْتَارْ مُوغَيٜىٰ، عَمَّا كَكَڢَ مَاسُ أَدَلْثِے، يَا اللَّهْ مَيْ أَدَلْثِے، كَيْ مَيْ عَوْنَ تُنَانِ دَ ظُكَاتَنْ مُتَنٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ka tsai da muguntar mugaye, Ina roƙonka, ka sāka wa mutanen kirki. Kai Allah mai adalci ne, Kana kuwa auna tunanin mutane, da marmarinsu.