Revelation 11:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
نَنْ تَكٜىٰ، سَيْ عَكَيِ وَتَ بَبَّرْ ضَوَرْ ڧَسَا، سَيْ كَشِ طَيَ بِسَ غُواْمَ نَبِرْنِنْ يَرُشٜىٰ، عَكَ كُمَ كَشٜىٰ مُتُمْ دُبُو بَݣَويْ؞ سَوْرَنْ مُتَنٜىٰنْ كُوَ سُكَجِڟُواْرُواْ ڨُورَيْ، سُكَ طَوْكَكَ اللَّهْ نَسَمَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A nan tāke sai aka yi wata babbar rawar ƙasa, sai ushirin garin ya zube, mutum dubu bakwai aka kashe a rawar ƙasar, sauran kuwa suka tsorata, suka ɗaukaka Allah Mai Sama.