Revelation 12:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan na ji babbar murya daga sama tana cewa, “Yanzu ceto da iko da mulkin Allahnmu, da kuma ikon Kiristinsa. Gama mai zargin ’yan’uwanmu, wanda yake zarginsu a gaban Allahnmu dare da rana, an jefar da shi ƙasa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْنَجِ وَتَ بَبَّرْ مُرْيَ أَ سَمَ تَنَ ثٜىٰوَ «يَنْذُ ڢَا، ثٜىٰتُواْ دَغَ اللَّهْ نْمُ، دَ إِيكُوانْسَ دَ مُلْكِنْسَ، دَ إِيكُوانْ أَلْمَسِيحُنْسَ سُنْثِكَ؞ غَمَا أَنْجٜىٰڢَرْ دَ مَيْ ڧَارَرْ یَنْعُوَنْمُ ڧَسَا، شِے دَيَكٜىٰ ڧَارَرْ یَنْعُوَنْمُ أَغَبَنْ اللَّهْ نْمُ دَرٜىٰ دَ رَانَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai na ji wata murya mai ƙara a Sama tana cewa, “A yanzu fa, ceto, da ƙarfi, da mulki na Allahnmu, da kuma ikon Almasihunsa sun bayyana, don an jefa mai ƙarar 'yan'uwanmu a ƙasa, shi da yake ƙararsu dare da rana a gun Allahnmu.