Revelation 15:3 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
suka rera waƙar Musa bawan Allah da kuma waƙar Ɗan Ragon suna cewa, “Ayyukanka suna da girma da kuma banmamaki, ya Ubangiji Maɗaukaki. Al’amuranka suna da aminci da kuma gaskiya, ya Sarkin zamanai.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُنَ رٜىٰرَ وَاڧَرْ مُوسَٰى، بَاوَنْ اللَّهْ دَ كُمَ وَاڧَرْ طَنْ ضَغُوانْ، سُنَ ثٜىٰوَ «أَيُّكَنْكَ دَ غِرْمَ سُكٜىٰ، مَاسُ بَنْ مَامَاكِ يَا عُبَنْغِجِ اللَّهْ مَيْ إِيكُواْ دُكَ! هَنْيُواْيِنْكَ مَاسُ أَدَلْثِے نٜىٰ، مَاسُ غَسْكِيَ كُمَ، يَا سَرْكِنْ أَلْعُمَّيْ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Suna raira waƙar da Musa bawan Allah ya yi, da kuma wadda ake yi wa Ɗan Ragon nan, suna cewa, “Ayyukanka manya ne, masu banmamaki, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki! Hanyoyinka na adalci ne, na gaskiya ne kuma, Ya Sarkin al'ummai.