Revelation 18:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ku ba ta isashen azaba da baƙin ciki kamar daraja da kuma jin daɗin da ta ba wa kanta. A zuciyarta takan yi taƙama, ta ce, ‘Ina zama kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taɓa yin makoki ba.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَمَرْ يَدَّ تَطَوْكَكَ كَنْتَ تَيِ رَايُوَرْ جِنْ دَاطِے كَوَيْ، حَكَ كُو مَا كُڠُودَ مَتَ عَذَابَ دَ بَڧِنْ ثِكِ ڠُورْڠُودُوانْ حَكَ؞ غَمَا ثِكِنْ ذُوثِيَارْتَ تَثٜىٰ، ‹نِے سَرَوْنِيَثٜىٰ عَكُجٜىٰرَرْ مُلْكِنَ! نِے بَمَاتَرْ دَ مِجِنْتَ يَمُتُ بَثٜىٰ، كُمَ بَذَنْ تَٻَيِنْ بَڧِنْ ثِكِيبَ!›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yadda ta ɗaukaka kanta, ta yi almubazzaranci, Haka ku ma ku saka mata da azaba, da baƙin ciki gwargwadon haka. Tun da yake a birnin zuciyarta ta ce, ‘Ni sarauniya ce, a zaune nake, Ni ba gwauruwa ba ce, Ba ni da baƙin ciki kuma har abada!’