Revelation 20:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Masu albarka da kuma tsarki ne waɗanda suke da rabo a tashin matattu na farko. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kansu, sai dai za su zama firistocin Allah da kuma na Kiristi za su kuma yi mulki tare da shi na shekaru dubu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مَاسُ أَلْبَرْكَ كُمَ مَاسُ ڟَرْكِے نٜىٰ وَطَنْدَ سُكٜىٰ دَ رَبُواْ ثِكِنْ وَنَّنْ ڢَرْكُوانْ تَاشِنْ مَتَتُّو؞ مُتُوَ تَبِيُ بَاتَدَ إِيكُواْ عَكَنْسُ، ذَاسُ ذَمَ ڢِرِسْتُواْثِنْ اللَّهْ دَ نَ أَلْمَسِيحُ ، ذَاسُ كُمَيِ مُلْكِ تَرٜىٰدَشِ حَرْ شٜىٰكَرُ دُبُو؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Duk wanda yake da rabo a tashin nan na farko, mai albarka ne, tsattsarka ne. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kan irin waɗannan, amma za su zama firistocin Allah da na Almasihu, su kuma yi mulki tare da shi har shekara dubu.