Romans 10:3 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُنْدَيَكٜىٰ بَسُ سَنْ حَنْيَرْ دَ اللَّهْ يَكٜىٰسَا مُتَنٜىٰ سُذَمَ مَاسُ أَدَلْثِبَ، كُمَ سُنَ ڧُواْڧَرِ سُكَڢَ تَاسُ حَنْيَرْ ذَمَ مَاسُ أَدَلْثِے أَغَبَنْ اللَّهْ ، سَيْ وَنَّنْ يَسَا بَسُ مِيڧَ كَنْسُ غَ حَنْيَرْ دَ اللَّهْ يَكٜىٰسَا مُتَنٜىٰ سُذَمَ مَاسُ أَدَلْثِبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Don saboda rashin fahimtar hanyar samun adalci, wadda Allah ya tanadar, da kuma neman kafa tāsu hanya, sai suka ƙi bin ita wannan hanya ta samun adalci wadda Allah ya tanadar.