Romans 11:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُواْ، إِنَ تَمْبَيَ، اللَّهْ يَڧِ مُتَنٜىٰنْسَ كٜىٰنَنْ؟ إِنَا! كُواْ كَطَنْ! نِے دَكَيْنَ مُتُمِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ نٜىٰ دَغَ ذُرِيَرْ إِبْرَٰهِيمْ، كُمَ مُتُمِنْ ذُرِيَرْ بِلِيَامِنُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
To, ina tambaya. Wato, Allah ya juya wa jama'arsa baya ke nan? A'a, ko kusa! Ai, ni ma da kaina Ba'isra'ile ne, zuriyar Ibrahim, na kabilar Biliyaminu.