Romans 5:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kyautar Allah kuwa ba kamar sakamakon da ya bi zunubin mutum gudan nan ba ne, Hukuncin ya bi zunubin mutum gudan nan, ya kuma kawo hallaka, amma kyautar ta bi laifofin masu yawa ta kuma sa Allah ya gan mu a matsayin marasa laifi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ڨُورَيْ كُوَ، ݣَوْتَرْ اللَّهْ دَبَمْ تَكٜىٰدَ ذُنُوبِنْ مُتُمْ طَيَنَّنْ؞ غَمَا حُكُنْثِنْدَ يَبِے بَايَنْ ذُنُوبِنَّنْ شِينٜىٰ حُكُنْثِنْ مُتُوَ، عَمَّا ݣَوْتَرْ دَ اللَّهْ يَبَايَرْ، عِتَثٜىٰ تَجَٰوُاْ مَنَ شَرِيعَرْ مَرَرْ لَيْڢِے أَغَبَنْسَ، كُواْدَيَكٜىٰ مُنْيِ ذُنُوبِ دَيَوَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Baiwar nan kuwa dabam take ƙwarai da hakkokin zunubin mutum ɗayan nan. Don kuwa hukuncin da aka yi a kan laifin mutum ɗayan nan, shi ya jawo hukuncin hallaka. Amma baiwar nan da aka yi a sanadin laifofi da yawa, ita take sa kuɓuta ga Allah.