Romans 5:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Gama in, ta wurin laifin mutum ɗaya, mutuwa ta yi mulki ta wurin mutum ɗayan nan, ashe, waɗanda suka sami kyautar alherin Allah a yalwace da kuma kyautar adalci za su yi mulki a wannan rayuwa ta wurin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تَوُرِنْ ذُنُوبِنْ مُتُمْ طَيَ، وَتُواْ ءَادَمُ، مُتُوَ تَيِ مُلْكِ عَكَنْ كُواْوَ، عَمَّا وَنَّنْ يِنْ مُلْكِ بَكُواْمٜىٰبَنٜىٰ عِدَنْ أَنْ‌ڠُودَاشِ دَ وَنْدَ مُتُمْ طَيَ، وَتُواْ عِيسَىٰ أَلْمَسِيحُ يَكَٰوُاْ غَ مَاسُ كَرْٻَرْ أَلْحٜىٰرِنْ اللَّهْ دَ ݣَوْتَرْسَ تَذَمَنْ أَدَلْثِے أَغَبَنْسَ؞ تَوُرِنْسَ نٜىٰ ذَاسُيِ مُلْكِ ثِكِنْ رَايُوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
In kuwa saboda laifin mutum ɗayan nan ne mutuwa ta yi mallaka ta wurinsa, ashe kuwa, waɗanda suke samun alherin nan mayalwaci, da kuma baiwar nan ta adalcin Allah, sai su yi mallaka fin haka ƙwarai a cikin rai, ta wurin ɗayan nan, wato Yesu Almasihu.