Romans 8:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
In kuwa mu ’ya’ya ne, to, mu magāda ne, magādan Allah da kuma abokan gādo tare da Kiristi, in kuwa muna tarayya a cikin shan wuyarsa to, za mu yi tarayya a cikin ɗaukakarsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَشٜىٰ، تُنْدَيَكٜىٰ مُو یَیَ نٜىٰ، مُنْ ذَمَ مَاسُثِنْ غَادُواْ كٜىٰنَنْ؞ وَتُواْ، مُو مَاسُثِنْ غَادُوانْ أَلْبَرْكُنْ اللَّهْ دَ كُمَ أَبُواْكَنْ غَادُواْ تَرٜىٰدَ أَلْمَسِيحُ نٜىٰ، عِدَنْ كُوَ مُنْ شَا وَهَلَ تَرٜىٰدَ أَلْمَسِيحُ ، دُواْمِنْ كُمَ أَطَوْكَكَمُ تَرٜىٰ دَشِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
In kuwa 'ya'ya muke, ashe, magāda ne kuma, magādan Allah, abokan gādo kuma da Almasihu, in dai har muna shan wuya tare da shi, a kuwa ɗaukaka mu tare da shi.