Ruth 1:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا رُوتْ تَا أَمْسَ مَتَ تَثٜىٰ «كَدَ كِيِ تَضُواْڧُواْنَ إِنْ كُواْمَ كُواْ إِنْ بَرْ بِنْكِ؞ غَمَا دُكْ عِنْدَ كِكَ تَڢِے، نَنْ ذَنْ تَڢِے؛ عِنْدَ كِكَ سَوْكَ، نَنْ ذَنْ سَوْكَ؞ مُتَنٜىٰنْكِ ذَاسُ ذَمَ مُتَنٜىٰنَ؛ كُمَ اللَّهْ نْكِ ذَيْ ذَمَ اللَّهْ نَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Rut ta ce, “Kada ki yi ta roƙona in rabu da ke, ko in bar binki, gama inda za ki tafi, ni ma can zan tafi, inda kuma za ki zauna, ni ma can zan zauna. Mutanenki za su zama mutanena, Allahnki kuma zai zama Allahna.