Zechariah 1:12 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً مَلاَىِٕكَنْ يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ «يَا يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا ، حَرْ يَوْشٜىٰ ذَاكَ دَيْنَ نُونَ جِنْڧَيْ غَ عُرُوشَلِيمَ دَ غَرُضُوً يَهُودَ؟ كَيِ تَجِنْ ڢُشِے دَسُو حَرْ شٜىٰكَرَا سَبَعِنْ! يَوْشٜىٰ ذَاكَ دَيْنَ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan mala'ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Runduna, har yaushe za ka ƙi nuna jinƙai ga Urushalima da biranen Yahuza, waɗanda kake jin haushinsu shekara saba'in ke nan?”