Zechariah 10:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Mutanen Efraim za su zama kamar mutane masu ƙarfi, zukatansu kuwa za su yi murna kamar sun sha ruwan inabi. ’Ya’yansu za su gani su yi murna; zuciyarsu za tă yi farin ciki a cikin Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ عَ أَرٜىٰوَ ذَاسُ ذَمَ كَمَرْ مَاسُ عِيَ يَاڧِ، ظُكَاتَنْسُ ذَاسُيِ ڢَضٍ ثِكِ كَمَرْ سُنْ شَا ضُوً إِنَبِے؞ عِ، یَیَنْسُ ذَاسُ غَنِ سُيِ مُرْنَ، ظُكَاتَنْسُ ذَاسُيِ ڢَضٍ ثِكِ ثِكِنْ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan mutanen Ifraimu za su zama kamar ƙarfafan jarumawa, Za su yi farin ciki kamar sun sha ruwan inabi, 'Ya'yansu za su gani su yi murna, Zukatansu za su yi murna da Ubangiji.