Zechariah 12:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«ذَنْ ظُبَ وَ ذُرِيَرْ دَاوُدَ دَ مَذَوْنَنْ عُرُوشَلِيمَ رُوحٌ تَوْسَيِ دَ نَأَدُّعَ؞ ذَاسُ دُوبٜىٰنِ، نِے وَنْدَ سُكَ سُواْكَ، سَعَنً ذَاسُيِ كُوكَا دُواْمِنَ كَمَرْ وَطَنْدَ عَكَيِ مُسُ مُتُوَرْ طَنْ ڢَارِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Zan cika zuriyar Dawuda da mutanen Urushalima da ruhun tausayi da na addu'a. Za su dubi wanda suka soke shi, har ya mutu. Za su yi makoki dominsa kamar waɗanda aka yi musu rasuwar ɗan farinsu.