Zechariah 7:5 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ka tambayi dukan mutanen ƙasar da firistoci cewa, ‘Sa’ad da kuka yi makoki da azumi a wata na biyar da na bakwai dukan shekaru saba’in nan, a ainihi saboda ni kuka yi azumi?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْ كَيْ وَ دُكَنْ مُتَنٜىٰنْ ڧَسَرْدَ ڢِرِسْتُواْثِے وَنَّنْ سَڧُواْ؞ يَثٜىٰ «أَوَطَنَّنْ شٜىٰكَرُ سَبَعِنْ نَذَمَنْ بَوْتَرْكُ، أَغَنِنْكُ، نُونَ بَڧِنْ ثِكِ تَوُرِنْ أَظُمِ وَنْدَ كُكَيِ عَكُواْوَنٜىٰ وَتَنْ بِيَرْ دَ نَبَݣَويْ دَ غَسْكٜىٰ سَبُواْدَنِنٜىٰ كُكَيِ وَنَّنْ أَظُمِ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
in faɗa wa dukan mutanen ƙasar da firistoci, in ce, “Sa'ad da kuka yi azumi da baƙin ciki a watan biyar da na bakwai dukan shekarun nan saba'in, saboda ni ne kuka yi azumin?