Zechariah 8:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Azumin wata na huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai da na watan goma za su zama lokutan farin ciki da murna da kuma bukukkuwa na murna ga Yahuda. Saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا ، ‹أَظُمِ نَوَتَنْ حُطُ دَ نَوَتَنْ بِيَرْ دَ نَوَتَنْ بَݣَويْ دَ نَوَتَنْ غُواْمَ، يَنْذُ ذَاسُ ذَمَ لُواْكَتَنْ مُرْنَ دَ ڢَضٍ ثِكِ؞ ذَاسُ ذَمَ بِكٍ ڢَضٍ ثِكِ غَ دُكَنْ غِدَنْ يَهُودَ؞ سَبُواْدَ حَكَ، سَيْ كُڧَوْنَثِ غَسْكِيَ دَ ذَمَنْ سَلَمَ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, azumi na watan huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai, da na watan goma, za su zama lokatan murna, da farin ciki, da idodin farin ciki, ga jama'ar Yahuza, saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.