Zechariah 8:3 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan koma Sihiyona in zauna a Urushalima. Sa’an nan za a kira Urushalima Birnin Gaskiya, a kuma kira dutsen Ubangiji Maɗaukaki Dutse Mai Tsarki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، ‹ذَنْ كُواْمَ تُدُنْ سِهِيُواْنَ، إِنْيِ ذَمَ أَڟَكِيَرْ بِرْنِنْ عُرُوشَلِيمَ؞ ذَاعَ ثٜىٰ دَ عُرُوشَلِيمَ بِرْنِ مَيْ أَمِنْثِ، بَبَّنْ تُدُنْ يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا ذَاعَ ثٜىٰ دَشِ بَبَّنْ تُدُ مَيْ ڟَرْكِے؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zan koma wurin Sihiyona, in zauna a tsakiyar Urushalima. Za a ce da Urushalima birnin gaskiya, da kuma dutsen Ubangiji Mai Runduna, tsattsarkan dutse.