Zechariah 9:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan ƙwace kekunan yaƙi daga Efraim, da kuma dawakan yaƙi daga Urushalima, za a kuma karya bakan yaƙi. Zai yi shelar salama ga al’ummai. Mulkinsa zai yaɗu daga teku zuwa teku, daga Kogi kuma zuwa ƙarshen duniya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
نِے يَهْوٜىٰهْ ، ذَنْ كَوَرْدَ كٜىٰكُنَنْ دُواْكِنْ يَاڧِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ، ذَنْ كُمَ كَوَرْدَ دَوَكِ دَغَ عُرُوشَلِيمَ؞ بَكَنْ يَاڧِ مَا ذَاعَ كَرْيَشِ؞ سَرْكِنْكُ ذَيْ كَٰوُاْ سَلَمَ غَ أَلْعُمَّيْ؞ مُلْكِنْسَ ذَيْ يَطُ دَغَ تٜىٰكُ ذُوَا تٜىٰكُ، دَغَ كُواْغِنْ يُڢِرٜىٰتِسْ حَرْ ذُوَا إِيَاكَرْ دُونِيَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce, “Zan datse karusa daga Ifraimu, In datse ingarman yaƙi a Urushalima, Zan kuma karya bakan yaƙi. Sarkinki zai tabbatar wa al'umman duniya da salama, Mulkinsa zai zama daga teku zuwa teku, Daga Kogin Yufiretis zuwa matuƙar duniya.”