Zephaniah 2:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَنَّنْ نٜىٰ بِرْنِ مَيْ تَاڧَمَ، وَنْدَ دَا يَذَوْنَ لَاڢِيَ، وَنْدَ يَثٜىٰ وَكَنْسَ، ‹نِے كَطَيْنٜىٰ، بَا وَنِ سَيْنِے!› غَاشِ، يَذَمَ كُڢَيْ، وُرِنْ ݣُونْثِيَرْ نَمُواْمِنْ دَاجِ! دُكْ وَنْدَ يَوُثٜىٰ تَوُرِنْسَ، ذَيْ يِڟَكِ، يَكَطَ كَيْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Wannan shi ne birnin da yake da harka, mai zaman lafiya, Wanda yake ce wa kansa, “Ba wani sai ni.” Ga shi, ya zama kufai, Wurin zaman dabbobi! Duk wanda ya wuce ta wurin, Zai yi tsaki, ya kaɗa kai.