Zephaniah 3:13 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Raguwar Isra’ila ba za su ƙara aikata abin da ba daidai ba, ba za su faɗa ƙarya ba, ba kuwa za a sami ruɗu a bakunansu ba. Za su ci su kuma kwanta kuma babu wanda zai ba su tsoro.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ضَغُواْوَرْ جَمَعَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ بَذَاسُ سَاكٜىٰ عَيْكَتَ مُغُنْتَا بَ، بَذَاسُ كُمَ ڢَطِ ڧَضْيَابَ، بَذَاعَ سَامِ ڧَضْيَا عَبَاكِنْسُبَ كُواْ رُوطُ أَ هَرْشٜىٰنْسُبَ؞ ذَاسُيِ كِيوُاْ، سُݣُونْتَ بَاوَنْدَ ذَيْ ڟُواْرَتَرْ دَسُو؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Waɗanda suka ragu cikin Isra'ila, Ba za su aikata mugunta ba, Ba kuma za su faɗi ƙarya ba, Gama harshen ƙarya ba zai kasance a bakinsu ba. Za su yi kiwo, su kwanta, Ba wanda zai tsorata su.”