bible
ra
🌐 Language
English
Español
Français
Deutsch
Português
Italiano
Nederlands
Русский
中文
日本語
한국어
العربية
Türkçe
Tiếng Việt
ไทย
Indonesia
All Languages
Home
/
Hausa
/
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
/
Nehemiah 7
Nehemiah 7
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
← Chapter 6
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 8 →
1
Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
2
Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
3
Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
4
Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
5
Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
6
Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
7
Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
8
Zuriyar Farosh mutum 2,172
9
ta Shefatiya 372
10
ta Ara 652
11
ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
12
ta Elam 1,254
13
ta Zattu 845
14
ta Zakkai 760
15
ta Binnuyi 648
16
ta Bebai 628
17
ta Azgad 2,322
18
ta Adonikam 667
19
ta Bigwai 2,067
20
ta Adin 655
21
ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
22
ta Hashum 328
23
ta Bezai 324
24
ta Harif 112
25
ta Gibeyon 95.
26
Mutanen Betlehem da na Netofa 188
27
na Anatot 128
28
na Bet-Azmawet 42
29
na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
30
na Rama da na Geba 621
31
na Mikmash 122
32
na Betel da na Ai 123
33
na ɗayan Nebo 52
34
na ɗayan Elam 1,254
35
na Harim 2 320
36
na Yeriko 345
37
na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
38
na Sena’a 3,930.
39
Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
40
ta Immer 1,052
41
ta Fashhur 1,247
42
ta Harim 1,017.
43
Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
44
Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
45
Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
46
Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
47
da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
48
da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
49
da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
50
da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
51
da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
52
da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
53
da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
54
da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
55
da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
56
da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
57
Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
58
da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
59
Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
60
Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
61
Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
62
zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
63
Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri ’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
64
Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
65
Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
66
Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
67
ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
68
Akwai dawakai 736, alfadarai 245
69
raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
70
Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
71
Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
72
Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
73
Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,
← Chapter 6
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 8 →
All chapters:
1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13