bible
ra
🌐 Language
English
Español
Français
Deutsch
Português
Italiano
Nederlands
Русский
中文
日本語
한국어
العربية
Türkçe
Tiếng Việt
ไทย
Indonesia
All Languages
Home
/
Hausa
/
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
/
Proverbs 21
Proverbs 21
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
← Chapter 20
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 22 →
1
A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
2
Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
3
Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
4
Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
5
Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
6
Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
7
Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
8
Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
9
Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
10
Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
11
Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
12
Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
13
In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
14
Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
15
Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
16
Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
17
Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
18
Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
19
Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
20
A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
21
Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
22
Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
23
Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
24
Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
25
Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
26
Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
27
Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
28
Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
29
Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
30
Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
31
Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
← Chapter 20
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 22 →
All chapters:
1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31