bible
ra
🌐 Language
English
Español
Français
Deutsch
Português
Italiano
Nederlands
Русский
中文
日本語
한국어
العربية
Türkçe
Tiếng Việt
ไทย
Indonesia
All Languages
Home
/
Hausa
/
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
/
Proverbs 31
Proverbs 31
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
← Chapter 30
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
1
Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
2
“Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
3
Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
4
“Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
5
don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
6
A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
7
bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
8
“Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
9
Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
10
Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
11
Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
12
Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
13
Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14
Ita kamar jirgin ’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
15
Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa ’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
16
Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
17
Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
18
Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
19
Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
20
Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
21
Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
22
Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23
Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
24
Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa ’yan kasuwa da ɗamara.
25
Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
26
Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
27
Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
28
’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
29
“Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
30
Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
31
Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.
← Chapter 30
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
All chapters:
1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31