bible
ra
🌐 Language
English
Español
Français
Deutsch
Português
Italiano
Nederlands
Русский
中文
日本語
한국어
العربية
Türkçe
Tiếng Việt
ไทย
Indonesia
All Languages
Home
/
Hausa
/
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
/
1 Chronicles 24
1 Chronicles 24
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
← Chapter 23
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 25 →
1
Ga yadda 'ya'yan Haruna, maza, suka karkasu. 'Ya'yan Haruna, maza, su ne Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar.
2
Amma Nadab da Abihu sun riga mahaifinsu mutuwa, ba su kuma da 'ya'ya. Saboda haka Ele'azara da Itamar suka shiga aikin firistoci.
3
Sai Dawuda da Zadok daga zuriyar Ele'azara, da Ahimelek daga zuriyar Itamar suka karkasa su bisa ga ƙayyadaddun lokatansu na yin aiki.
4
Tun da yake akwai manyan mutane da yawa a zuriyar Ele'azara fiye da zuriyar Itamar, sai suka karkasa su haka, shugabannin gidajen kakannin zuriyar Ele'azara mutum goma sha shida, na zuriyar Itamar kuwa su takwas, bisa ga gidajen kakanninsu.
5
Da haka aka karkasa su ta hanyar kuri'a gama akwai ma'aikatan Wuri Mai Tsarki da kuma ma'aikata na Allah daga zuriyar Ele'azara da zuriyar Itamar.
6
Shemaiya, ɗan Netanel marubuci, Balawe, ya rubuta su a gaban sarki da shugabanni, da Zadok firist, da Ahimelek ɗan Abiyata, da shugabannin gidajen kakannin firistoci, da Lawiyawa. Aka ɗauki gida guda daga gidajen kakannin Ele'azara, aka kuma ɗauki ɗaya daga gidajen kakannin Itamar.
7
Ga yadda aka shirya ƙungiyoyin iyali ashirin da huɗu su sami aikinsu, 1) Yehoyarib, 2) Yedaiya, 3) Harim, 4) Seyorim, 5) Malkiya, 6) Mijamin, 7) Hakkoz, 8) Abaija, 9) Yeshuwa, 10) Shekaniya, 11) Eliyashib, 12) Yakim, 13) Huffa, 14) Yeshebeyab, 15) Bilga, 16) Immer, 17) Hezir, 18) Haffizzez, 19) Fetahiya, 20) Yehezkel, 21) Yakin, 22) Gamul, 23) Delaiya, 24) Ma'aziya.
19
Waɗannan suna da aikin da aka ba su na hidimar Haikalin Ubangiji bisa ga ka'idar da kakansu Haruna ya kafa musu, kamar yadda Ubangiji Allah na Isra'ila ya umarce shi.
20
Sauran 'ya'yan Lawi, maza, na wajen Amram, shi ne Shebuwel. Na wajen Shebuwel, shi ne Yedaiya.
21
Na wajen Rehabiya, shi ne Isshiya,
22
Na wajen Izhara, shi ne Shelomit, na wajen Shelomit, shi ne Yahat.
23
Na wajen Hebron, su ne Yeriya na fari, da Amariya, da Yahaziyel, da Yekameyam.
24
Na wajen Uzziyel, shi ne Mika, na wajen Mika, shi ne Shamir.
25
Ɗan'uwan Mika, shi ne Isshiya. Na wajen Isshiya, shi ne Zakariya.
26
Na wajen Merari, Mali da Mushi, da Yayaziya. Na wajen Yayaziya, shi ne Beno.
27
Na wajen Merari, wato na wajen Yayaziya, su ne Beno, da Shoham, da Zakkur, da Ibri.
28
Na wajen Mali, shi ne Ele'azara wanda ba shi da 'ya'ya maza.
29
Na wajen Kish, ɗan Kish, shi ne Yerameyel.
30
'Ya'yan Mushi, maza, su ne Mali, da Eder, da Yerimot. Waɗannan su ne 'ya'yan Lawiyawa, maza, bisa ga gidajen kakanninsu.
31
Su ma suka jefa kuri'a kamar yadda 'yan'uwansu, 'ya'yan Haruna, maza, suka yi a gaban sarki Dawuda, da Zadok, da Ahimelek, da shugabannin gidajen kakanni na firistoci da na Lawiyawa. Shugaban gidan kakanni ya jefa kuri'a daidai da ƙanensa.
← Chapter 23
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 25 →
All chapters:
1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29