bible
ra
🌐 Language
English
Español
Français
Deutsch
Português
Italiano
Nederlands
Русский
中文
日本語
한국어
العربية
Türkçe
Tiếng Việt
ไทย
Indonesia
All Languages
Home
/
Hausa
/
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
/
Job 5
Job 5
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
← Chapter 4
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 6 →
1
“Ka yi kira, ya Ayuba, ka gani, ko wani zai amsa! Akwai wani mala'ika da za ka juya zuwa gare shi?
2
Ba shi da amfani ka dami kanka Har ka mutu, saboda tsarguwa, gama wannan wawanci ne, Da aikin rashin hankali.
3
Na ga waɗansu wawaye waɗanda ake gani kamar suna zaune lafiya, Amma nan da nan sai na la'anci gidajensu.
4
Ko kaɗan, 'ya'yansu maza ba za su taɓa zama lafiya ba. Ba wanda zai tsaya musu a ɗakin shari'a.
5
Mayunwata za su ci amfanin gonar wawa, Har da hatsin da yake girma cikin ƙayayuwa, Waɗanda suke jin ƙishirwa za su ji ƙyashin dukiyarsa.
6
Zunubi ba ya tsirowa daga ƙasa, Haka ma wahala ba ta tsirowa daga ƙasa.
7
Ai, an haifi mutum domin wahala ne, Tabbatacce ne kamar yadda tartsatsin wuta suke tashi.
8
“In da ni ne kai, da sai in juya wurin Allah, In kai ƙarata a wurinsa.
9
Ba za mu iya fahimtar manyan abubuwa da yake yi ba, Al'ajabansa kuwa ba su da iyaka.
10
Yakan aiko da ruwan sama, Ya shayar da gonaki.
11
I, Allah ne yake ɗaukaka masu tawali'u, Shi yake kuɓutar da dukan waɗanda suke makoki.
12
Yakan birkitar da shirye-shiryen masu wayo.
13
Yakan sa wa masu wayo tarko cikin dabarunsu, Har ba za su yi nasara a dukan abin da suke yi ba.
14
Da rana sukan yi karo da duhu, Ko da tsakar rana ma lalube suke kamar ana duhu.
15
Amma Allah yakan ceci matalauta daga mutuwa, Yakan kuma ceci masu bukata daga zalunci.
16
Yakan sa matalauta su sa zuciya, Ya sa mugaye su yi shiru.
17
“Mai farin ciki ne mutumin da Allah ya hora, Kada ka tsargu sa'ad da ya tsauta maka.
18
Allah yakan yi maganin raunin da ya yi maka, Ciwon da ya ji maka da hannunsa, Da hannunsa yakan warkar.
19
Yakan tsare ka daga cuta sau shida har sau bakwai, Ba muguntar da za ta taɓa ka.
20
Yakan kiyaye ka da rai a lokacin yunwa, A yaƙi kuma yakan tsare ka daga mutuwa.
21
Allah yakan kuɓutar da kai daga ƙarairayi da ɓata suna, Yakan cece ka daga hallaka.
22
Aikin kama-karya da yunwa za su zama abin dariya a gare ka, Ba kuwa za ka ji tsoron namomin jeji ba.
23
Ba za a sami duwatsu a gonakin da kake nomawa ba, Mugayen namomin jeji ba za su far maka ba.
24
Sa'an nan za ka zauna lafiya a alfarwanka, A sa'ad da ka dubi tumakinka, za ka tarar suna nan lafiya.
25
'Ya'yanka za su yi yawa kamar ciyawa, Kamar yadda alkama take a lokacin kakarta.
26
Haka kai ma za ka rayu, har ka tsufa da kyakkyawan tsufa.
27
Kai, Ayuba, mun koyi wannan don mun daɗe muna nazari, Gaskiya ce, don haka ka yarda da wannan.”
← Chapter 4
Jump to:
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 6 →
All chapters:
1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42